Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Wani Shehin Malamin Jami'a Ya Ce Talakawa Na Tasirin Wajen Ayyukan Da Gwamnati Ke Masu


Wasu talakawa da ke bukatar gwamnatinsu ta gyara masu muhalli
Wasu talakawa da ke bukatar gwamnatinsu ta gyara masu muhalli

Talakawa ma su na taka rawa wajen samar ma gwamnati sukunin taimaka masu ta wajen hada kai da tabbatar da kwanciyar hankali don hukuma ta yi aiki, in ji wani sheihin malamin jami'a.

Wani furfesan jami’a y ace duk wata jam’iyya a Nijeriya wace ta ce ta na so ta kawo cigaban Nijeriya amma ba ta yi wani abu ba na a zo a gani a fannin rayuwar mutane kamar iliminsu da lafiyarsu da sauransu - wadanda su ke kawo cigaba ba – to abin takaici ne. Y ace muddun aka kyautata rayuwar mutane to kasa za ta samu cigaba sosai. Y ace muddun akasarin mutanen kasa ba a inganta rayuwarsu, saidai kawai a je a kawo kamfanonin kasashen waje su yi harkar mai, idan kuma an sayar a raba ma jihohi, kuma jihohin su kasa yin komai, babu inda za a je.

Furfesa Samuel Zalanga, wanda abokiyar aikinmu Grace Alheri Abdu ta zanta da shi, y ace koda yak e an sami ‘yanci fiye da shekaru 50 da su ka gabata an kasa samun cigaba saboda an kasa inganta rayuwar ‘yan kasa wanda shi ne kan gaba. Y ace kuma idan jam’iyyar siyasa za ta kawo cigaba ga al’umma to kar ta nuna banbancin addini ko na siyasa ko na kabila ko na jinsi.

Y ace yadda su kuma talakawa za su taka rawa wajen kawo cigabansu shi ne ta hada kawunansu don a sami zaman lafiya da kwanciyar hankalin da ake bukata. Y ace kodayake akwai banbancin addini da na kabila da na siyasa tsakanin jama’a, dole ne dai jama’a su hada kawunansu kafin hukuma ta sami cikakken sukunin kawo cigaba.

please wait

No media source currently available

0:00 0:03:46 0:00
Shiga Kai Tsaye

Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG