Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Wasu 'Yan Siyasa Sun Yaba da Zaben Bana


Yanzu haka dai ana nan ana tattara sakamakon zabe, amma ya zuwa lokacin da muka sami wannan rahoton akwai rumfunan da ake cigaba da jefa kuri’a a jihohin Sokoto da Kebbi.

Duk da tsaikon da aka samu da kuma wasu ‘yan matsaloli da aka fuskanta musamman da na’urar tantance katin zabe da ma kamala zabe a makare a wasu rumfuna a jihohin Sokoto da Kebbi da Zamfara, ‘yan siyasa da masu zabe sun bayyana gamsuwarsu da sabon tsarin gudanar da zabe.

Sanata Abdallah Wali dan takarar gwamna na jam’iyyar PDP a jihar Sokoto, shi ma ya bayyana gamsuwarsa da sabon tsarin, abinda yace zai magance matsalar magudin zabe dake addabar tsarin zabe a Najeriya.

Ita ma jam’iyyar Adawa ta APC ta jinjinawa hukumar zaben Najeriya akan sabon tsarin. Sani Hukuma Zauro, babban jigo ne a jam’iyyar APC a jihar Kebbi shima ya yabawa shugaban hukumar zabe Alhaji Attahiru Jega saboda sabon tsarin.

Baki daya dai an gudanar zabukan shugaban kasa da na 'yan majalisa salun alun a jihohin Sokoto Kebbi da Zamfara duk da cewa dai an ba’a fara zabe da wuri ba a wasu rumfunan.

please wait

No media source currently available

0:00 0:02:50 0:00
Shiga Kai Tsaye

XS
SM
MD
LG