Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Wata Kungiyar Kare Hakin Bil'adama Tana Kalubalantar Katse Hanyoyin Wayar Salula A Najeriya


Wata Mace tana waya a gona
Wata Mace tana waya a gona
Babbar kotun tarayya dake zama a garin Gombe ta fara sauraron karar da gamayyar kungiyoyin ‘yancin dan adam wato Civil Rights Congress ta shigar gabanta, inda kungiyar ke kalubalantar gwamnatin Tarayyar Najeriya da kuma kamfanonin wayar salula a kasar bisa yanke hanyoyin sadarwa a jihohin da gwamnatin tarayya ta kafa dokar- ta-baci.

Bayan sauraron bahasi daga lauyan masu shigar da karar ne alkalin kotun mai shari'a Baba Tunde Kadiri ya shawarci lauyan yayi wadansu ‘yan gyare- gyare a takardar da ya gabatar na shigar da karar.

Bayan zaman sauraron bahasin wakilinmu a shiyar Bauchi Abdulwahab Muhammad ya zanta da lauyan dake wakiltar kungiyar Barrister Luka Musa Haruna.
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:32 0:00
Shiga Kai Tsaye
  • 16x9 Image

    Grace Alheri Abdu

    Grace Alheri Abdu  babbar Edita ce (Managing Editor) a Sashen Hausa na Muryar Amurka wadda ta shafe sama da shekaru 30 tana aikin jarida. Tana da digiri na biyu a fannin dokoki da huldar diplomasiyar kasa da kasa, da kuma digiri na biyu a fannin nazarin addinan al'adun gargadiya na kasashen Afrika.

XS
SM
MD
LG