Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

‘Yan Fansho Na Bin Gwamnatocin Jihohinsu Bashin Makuden Kudade


'Yan fansho a jihar Kano
'Yan fansho a jihar Kano

Tsoffin ma’aikata ‘yan fensho dake jihohin Arewa maso Gabas, sunce suna bin gwamnatocinsu kudaden fensho da garatuti fiye da Naira Miliyan Dubu Dari.

An bayyana hakan ne a karshen taron shugabanin kungiyar yan fensho na jihohin Arewa maso Gabas a Bauchi. Mataimakin shugaban ‘yan Fansho na wannan shiyya Mohammad Inuwa Ahmed Dan, yace halin da ‘yan Fanshon ke fuskanta a Najeriya shine dalilin taron da Bauchi, ya kuma nuna cewa wasu jihohi kan yi iyaka kokarinsu na ganin sun biya kudaden da ake binsu amma wasu basa kokari ko kadan.

Taron dai na jawo hankulan gwamnatocin da cewa su tuna cewar ‘yan Fanshon nan mutane ne da suka bautawa ‘kasa, kuma suyi la’akari da yawan da ‘yan fensho domin zasu iya nuna banbanci a lokacin zabe.

Shugaban kungiyar masu karbar Fansho a jihar Taraba Kwamarad Hassan Abubakar, yace matsalolin kusa ‘daya ne a dukkannin jihohin sai dai a Tarabar akwai dan banbanci.

Saurari cikakken rahotan.

please wait

No media source currently available

0:00 0:03:08 0:00

Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG