Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

'Yan Najeriya 200,000 Ke Gudun Hijira a Jamhuriyar Nijar


'Yan gudun hijira sandiyar hare-haren 'yan Boko Haram
'Yan gudun hijira sandiyar hare-haren 'yan Boko Haram

Kimanin 'yan Najeriya dubu dari biyu ke gudun hijira a Jamhuriyar Nijar bayan hare-hare da yankunansu su ka yi fama da su.

Gwamnan jihar Diffa ta Jamhuriyar Nijar Alhaji Usman Gawo ya ce kafin a kai harin Baga suna da 'yan gudun hijira daga Najerya kimanin dubu dari da hamsin. To amma yanzu adadinsu ya kai dubu dari biyu.

A cewar gwamnan jihar, sa ce ke daukan nauyin cinsu da shansu da ma kulawa da harkokin lafiyarsu sanadiyar taimakon da gwamnatin kasar Nijar da masu hannu da shuni ke bayarwa.

Mafi yawan 'yan gudun hijiran 'yan jihar Borno ne. Gwamnan Bornon Kashim Shettima ya ce suna shirin mayar da mutanen garuruwansu muddin an samu zaman lafiya amma sai gwamnati ta gama gyaran gidajensu da asibitoci da makarantu da ruwan sha tare da tanadar masu da abinci.

Su ma 'yan gudun hijiran sun ce sun fi so su koma garuruwansu.

Ga karin bayani.

please wait

No media source currently available

0:00 0:06:23 0:00
Shiga Kai Tsaye

XS
SM
MD
LG