Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

'Yan Najeriya Na Kyakkyawan Zato Ga Gwamnati a Sabuwar Shekarar 2016


Shugaban Najeriya, Muhammadu Buhari
Shugaban Najeriya, Muhammadu Buhari

Mutane da yawa na ci gaba da tofa albarkacin bakinsu game da mulkin shugaban Najeriya Muhammadu Buhari musamman in suka yi la'akari da shekarar data shude ta 2015.

Kasan cewar an shiga sabuwar shekarar 2016 ne, sai wasu 'yan Najeriya suka tofa albarkacin bakinsu game da shekarar 2015 da ta shude na dadi ko wuyar da ke cikinta.

Mafiya yawan wadanda suka yi magana sun yi bayani ne ta bangaren wahalar rayuwa a kasar musamman a bangaren illar da rashin kyakkyawan shugabanci ya haifa.

Wanda suke ganin ma a yanzu haka ana kokarin shawo kan matsalolin da sabuwar gwamnatin ta gada daga tsohuwar gwamnatin da ta shude ta Shugaba Goodluck Jonathan.

Tun dai zuwan sabuwar gwamnatin ne mutane ke ta tofa albarkacin bakinsu, wasu su ce sam barka wasu kuma su ce tir. Inda masana siyasa daban daban suka dunga tsokaci.

Ga Wakilin sashen Hausa Abdulwahab Muhammad daga Bauchi a Najeriya da wannan rahoton cikin murya.

please wait

No media source currently available

0:00 0:02:11 0:00

XS
SM
MD
LG