Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

An Bukaci Al'umar Kasar Nijar Sun Gudanar Da Zabe Cikin Kwanciyar Hankali


Tambarin Jamhuriyar Nijar
Tambarin Jamhuriyar Nijar

Wadanda hakkin zabe ya rataya akansu su fito su zabi abinda zai zama alheri ga kasar Nijar

A yayin da ya rage kwanaki a gudanar zaben shugaban kasa da na ‘yan majalisu a jamhuriyar Nijar, ‘yan Nijar Mazauna Najeriya, sun bukaci al’umar kasar ta Nijar, dasu gudanar ta zaben cikin kwanciyar hankali da lumana.

Wani Mazaunin Ibadan Alhaji Janaidu Mai Shayi, yace “ maza da mata ‘yan Nijar wadanda hakkin zabe ya rataya akansu su fito su zabi abinda zai zama alheri ga kasar Nijar”.

Shima Mahmuda Nijar Tawa, cewa yayi fatan su shine ayi zabe lafiya a gama lafiya duk wanda Allah ya baiwa a mika mashi batare da wani fitina ba.

Shima Muhammadu Lawal, cewa yayi yana fatar zaben da za’a gudanar ya kasance an zabi shugaba na gari, mai adalci mai tausayin talakawane kuma Allah yasa ya kasance mai kishin kasa ne.

please wait

No media source currently available

0:00 0:01:55 0:00

XS
SM
MD
LG