Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

'Yan Nijeriya na Cigaba da Kiran Gwamnatin Kasar ta Dau Mataki Kan Wadanda Ake Zargi da Tallafawa 'Yan Boko Haram


Wasu sojojin Nijeriya na fafatawa da Boko Haram.
Wasu sojojin Nijeriya na fafatawa da Boko Haram.

A Nijerya an cigaba da kiraye kirayen gwamnati ta dau mataki kan wadanda Baturen Australia din nan mai suna Stephen Davis ya zarga da taimakawa 'yan Boko Haram.

Kungiyoyi da daidaikun ‘yan Nijeriya na cigaba da kiraye-kirayen gwamnatin Nijeriya ta dau mataki kan mutanen da Baturen Australia Stephen Davis y ace sun a taimakawa ma Boko Haram.

Alhaji Ibrahim Garba Wala ya ce kamar yadda Baturen na kasar Australia ya taimaka da bayani, su ma a matsayinsu na ‘yan Nijeriya za su taimaka wajen ankarar da gwamnatin Nijeriya muhimmancin binciken wadanda aka zarga din. Y ace binciken shi zai nuna ko sun aikata ko kuma a’a; zai kuma nuna ko da Karin wasu da ke taimakawa ‘yan Boko Haram din ko a’a.

Shi ko Baballe Sarkin Hausawan Kuma kuma Shugaban Kungiyar Rundunar Adalci ta Gombe y ace kamata ya yi a rinka gaya ma Shugaban kasa gaskiya a irin halin da ake cikin a maimakon labaran siyasa.

Shi ma a nasa ra’ayin, sanannen lauyan nan mai tsokaci kan al’amuran zamantakewa da siyasa, Barrister Solomon Darlong, yace daga kuduncin Nijeriya ne aka kirkiro kungiyar Boko Haram aka cinna ma arewa don a kassara ta. Y ace an yi ta samun ‘yan kudancin Nijeriya da hannu a hare-haren da aka yi ta kaiwa da sunan Boko Haram. Don haka y ace an fara Boko Haram ne da sunan addini amma daga baya sai ya rikide ya zama na siyasa.

please wait

No media source currently available

0:00 0:04:00 0:00
Shiga Kai Tsaye

XS
SM
MD
LG