Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Shugaba Obama Da Mr. Romney Sun Yi Yakin Neman Zabensu Na Karshe.


Mr. Romney da shugaba Obama a muhawararsu ta karshe.
Mr. Romney da shugaba Obama a muhawararsu ta karshe.
A jajiberen babban zabe a nan Amurka, shugaba Barack Obama na Amurka da dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Republican dake kalubalantarsa, Mitt Romney, sun yi yakin neman zabe na karshe a muhimman jihohin da sune zasu iya shata wanda zai lashe wannan zabe na yau talata, wanda har yanzu babu wanda yayi ma wani fintinkau a cikinsu.

A Jihar Wisconsin, shugaba Obama ya zargi Mr. Romney da kokarin yin ado ma munanan manufofin da ‘yan Republican suka aiwatar a can baya, yana mai cewa kasar nan ba zata samu nasara ba har sai ta bunkasa al’ummar dake tsaka tsaki

Zamu ci gaba da gwagwarmayarmu a saboda mun san Amurka a koda yaushe tana bunkasa. Muna samun gawurta a duk lokacin da aka ba kowa dama, a duk lokacin da kowa ya dafa daidai wa daida, kuma a duk lokacin da kowa ke aiki da ka’idoji iri daya.

Abinda muka yi imani ke nan. Wannan shi yasa kuka zabe ni a 2008, kuma wannan shi ne dalilin da yasa nake neman wa’adi na biyu a matsayin shugaban Amurka.
A wajen wani gangamin da yayi da sanyin safiyar jiya a Jihar Florida, Mr. Romney ya fadawa magoya bayansa cewa shugaban dan jam’iyyar Democrat, ya kasa cika alkawuran da yayi har ya ci zaben 2008.

Shugaban nan yayi alkawarin kawo canje-canje masu yawa, amma ai ba iya jawabi ne canji ba. Ana auna canji ne ta hanyar nasarorin da mutum zai gani a kasa. Shekaru hudu da suka shige, Obama yayi alkawura da yawa lokacin da yake takara, amma kuma kash, har yanzu ya kasa cimma su.

Masu fashin bakin siyasa a nan Amurka suka ce daga cikin jihohi guda hamsin na Amurka, ‘yan kalilan ne kawai zasu iya fayyace wanda zai ci zaben na yau talata, a saboda akasarinsu an riga an san ko dai shugaba Obama ko Mr. Romney ne zasu lashe su. ‘Yan jihohin da har yanzu ba a san wanda zai lashe su ba, sune ake yakin neman zabe kansu gadan gadan. Zaben shugaban kasa na Amurka, ba wai ana yinsa ne ta kirga illahirin kuri’un da aka kada domin ganin mai rinjaye ba, ana yinsa ne bisa tsarin zaben wakilai ko mazaba wadanda sune a zahiri zasu zabi shugaban kasa. Yawan wakilai ko mazaba na kowace jiha, ya danganci yawan jama’arta idan an kwatanta da sauran jihohin kasa.

A bayan gangamin da yayi a Wisconsin, shugaba Obama ya yada zango a Jihar Ohio, kafin ya zarce zuwa Jihar Iowa, inda a yanzu haka yake gudanar da yakin neman zabensa na karshe. Mr. Romney ya yada zango a Ohio da Jihar Virginia, sannan ya zarce zuwa Jihar New Hampshire.
Miliyoyin jama’a a kasar nan dai sun riga sun kada kuri’unsu karkashin dokokin jefa kuri’a da wuri a wasu jihohi. Amma mafi yawan masu jefa kuri’a yau ne zasu doshi rumfunan zabe da za a kakkafa a makarantu da gidajen ‘yan kwana-kwana da coci-coci.

Kuri’un neman ra’ayoyin jama’a dabam-dabam sun nuna ‘yan takarar biyu su na kunnen doki a kasa. Amma a kuri’un neman ra’ayoyin masu jefa kuri’a a jihohi guda 9 wadanda sune zasu tantance wanda zai lashe wannan zabe, sun nuna shugaba Obama yana kan gaba a akasarinsu, amma da ‘yar rata kadan. Romney yana kan gaba a cikin jiha kwaya daya tak ne daga cikin wadannan jihohi, watau a Jihar Florida.
Wata manhaja mai saukaka wahalar samun gidan abinci na halal ga Musulman dake zaune a kasashen Turai
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:21 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG