Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

'Yan Tawaye Sun Kwace Ikon Babban Birnin Damokaradiyar Janhuriyar Afrika Ta Tsakiya


Sojojin Damokaradiyar Jamhuriyar Afrika ta Tsakiya
Sojojin Damokaradiyar Jamhuriyar Afrika ta Tsakiya
‘Yan tawayen jamhuriyar Afrika ta Tsakiya sun kwace ikon babban birnin kasar abinda ya tilasawa shugaban kasar Francois Bozize arcewa daga Bangui.

Shaidu sun bada rahoton jin karar manyan makaman fada a birnin da asubahin yau Lahadi yayinda ‘yan tawayen suke kutsawa babban birnin kasar, a kan hanyarsu zuwa kwace ikon fadar shugaban kasa.

Hukumomi basu bayyana a hukumance inda shugaba Bozize ya gudu ba. Kamfanin dillancin labarai na Reuters ya ambaci ta bakin wani mai ba shugaban kasa shawarwari da ya nemi a saya sunansa cewa, shugaban kasar ya ketara zuwa Damokaradiyar Jamhuriyar Kwango yau Lahadi da asuba.

Da farko ‘yan tawayen sun kutsa Bangui jiya asabar suka yi watsi da da kiran da Firai Ministan kasar ya yi da su zauna a tattauna da nufin gudun zubar da jinni.

Tun farko jiya asabar a cikin hira da sashen Farasanci na wannan tashar wani kakakin gwamnatin yace, Firai Minista Nicolas Tiangaye ya yi kira ga kungiyar ‘yan tawaye ta Seleka Alliance ta tuntubi gwamnatin hadin guiwa ta kasar domin shawo kan matsalar ta hanyar lumana. Sai dai ‘yan tawayen Seleka sun ce ba zasu tattauna ba sai shugaba Bozize ya sauka daga karagar mulki.
  • 16x9 Image

    Grace Alheri Abdu

    Grace Alheri Abdu  babbar Edita ce (Managing Editor) a Sashen Hausa na Muryar Amurka wadda ta shafe sama da shekaru 30 tana aikin jarida. Tana da digiri na biyu a fannin dokoki da huldar diplomasiyar kasa da kasa, da kuma digiri na biyu a fannin nazarin addinan al'adun gargadiya na kasashen Afrika.

Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG