Saudiyya da Birtaniya sun tabbatar da haka. Shi kansa matukin jirgin shima ya mutu. Jakadan Saudi a Birtaniya yayi amfani da shafin sun a Twitter wajen mika ta’aziyyarsa ga iyalan Bin Laden.
Sai dai bai bayyan sunayen wadanda suka mutun ba. Ofishin jakadanci Saudi a Ingilar zai binciki musabbabin hatsari sannan zai danka gawarwakinsu har Saudi.
Jakadan Saudin Yarima Mohammed Bin Nawaf Bin Aldelaziz ne ya bayyana haka. Suma ‘yan sanda sun bayyana cewa jirgin ya fadi ne a kusa da ma’ajiyar motocin da akan gwanjonsu.
Bayan ya fadi kuma ne ya kama da wuta, duk a kokarin sauka a filin jiragen saman Blackbushe dake nisan kilomita 65 daga kudu maso yammacin Landan bayan tasowarsa daga filin jirgin Melpensa dake birnin Milan.