Wadanda ake zargin kuma suna da alaka da kungiyar mayakan sakai ta al-Shabab dake Somaliya.
Jiya lahadi,’Yan Sanda suka ce sun kai somamen ne da safiyar lahadi a wani gida dake wajajen fitar birnin Mombasa,a birnin ne babbar tashar jiragen ruwan kasar take.
Jami’ai suka ce an kashe daya daga cikin mutanen a cikin gidan, yayinda na biyun kuma, ya gamu da ajalinsa lokacinda yake kokarin gudu.
Wannan somamen shine na baya bayan nan, a fito na fito da ake tayi tsakanin ‘Yan Sanda, da masu kishin addini, da ‘yan aware dake kan gabar teku a kasar.
Magoya bayan al-Shabab sun sha kai hare hare domin nuna adawarsu da shawarar da Kenya ta yanke na tura sojoji zuwa Somalia, domin su yaki mayakan sakai masu zazzafar ra’ayi.
Jiya lahadi,’Yan Sanda suka ce sun kai somamen ne da safiyar lahadi a wani gida dake wajajen fitar birnin Mombasa,a birnin ne babbar tashar jiragen ruwan kasar take.
Jami’ai suka ce an kashe daya daga cikin mutanen a cikin gidan, yayinda na biyun kuma, ya gamu da ajalinsa lokacinda yake kokarin gudu.
Wannan somamen shine na baya bayan nan, a fito na fito da ake tayi tsakanin ‘Yan Sanda, da masu kishin addini, da ‘yan aware dake kan gabar teku a kasar.
Magoya bayan al-Shabab sun sha kai hare hare domin nuna adawarsu da shawarar da Kenya ta yanke na tura sojoji zuwa Somalia, domin su yaki mayakan sakai masu zazzafar ra’ayi.