Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Yau Amurkawa ke tunawa da ML King wanda yayi fafutukar nemar ma bakake 'yanci


Martin Luther King, Jr. yayinda yake shahararren jawabinsa da ya taba zukatan mutane har aka ba bakake cikakken 'yanci, a garin Selma, jihar Alabama, Feb. 12, 1965.
Martin Luther King, Jr. yayinda yake shahararren jawabinsa da ya taba zukatan mutane har aka ba bakake cikakken 'yanci, a garin Selma, jihar Alabama, Feb. 12, 1965.

Yau Litinin Amurkawa a duk fadin kasar na hutu domin tunawa da ranar da aka haifi Shugaban fafutar samar da cikakken ‘yan ci wa bakake da sauran jinsin da ba turawa ba ne, wanda aka kashe, wato Martin Luther King Junior.

A dai shekarar 1955 King ya samu daukaka, bayan da ya jagoranci wani borin kauracewa shiga motocin sufuri na Bas a kudancin birnin Montgomery dake jihar Alabama, lamarin da ya tilsatawa hukumomin birnin kawo karshen tsarin nan da ke kebe fasinjoji bakaken fata.

A kuma shekarun 1950s da 60s, King ya zama jigon fafutukar neman ‘yan cin da shahararren jawabinsan nan mai taken “ I Have A Dream” wanda ya ja hankulan miliyoyin mutane a lokacin da ya gabatar da shi a wani gangami ko kuma maci da aka yi a nan Washington a shekarar 1963.

A shekarar 1964 ya karbi lambar yabon nan ta zaman lafiya, ko kuma Nobel Peace Prize, a kuma shekararce shugaba Lyndon Johnson ya saka hannu a dokar nan da ta tabbatar da samar da cikakken ‘yan ci ga mutanen da ake nunawa wariya musamaman bakaken fata.

A ranar hudu ga watan Aprilun shekarar 1968 aka kashe King a birnin Memphis dake jihar Tennessee, a lokacin da ya je ya taimakawa bakaken fata masu kwasar shara a fafutukar da su keyi ta neman a daidaita musu albashin su da sauran ma’aikata.

A shekarar 1983 shugaba Ronald Reagan ya saka hanu a wata doka da ta umurci a rika ware duk ranar Litinin ta uku a watan Janairu a matsayin ranar karrama Martin Luther King, wanda aka haifa a ranar 15 ga watan Janairun 1929.

XS
SM
MD
LG