Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Yau Ce Ranar Nakasassu Ta Duniya


Yusuf Umar (Dama) da Aminu Ahmed da suka samu nakasa dalilin cutar polio
Yusuf Umar (Dama) da Aminu Ahmed da suka samu nakasa dalilin cutar polio

Yau ce Ranar da Majalisar Dinkin Duniya ta ware domin yin dubi kan irin halin da nakasassu ke ciki a duk fadin duniya.

Taken wannan shekara shi ne cimma muradi na 17 da aka shata domin samun makoma ta gari ga masu nakasa.

Wannan rana akan yi bkin ta ne da gudanar da taruka da liyafa da kuma ziyara zuwa gidajen masu fama da nakasa a duk fadin duniya.

“Mu yi aiki tare domin ta yadda masu fama da nakasa za su gurbin a dama da su a kowane fannin rayuwa dake rungumar kowane dana dam koda daga ina ya fito.” In ji Babban Sakataren Majalisar Dinkin Duniya, Ban Ki-moon.

Domin jin yadda wannan rana ta gudana a wasu sassan Najeriya da Nijar, saurari rahotannin wakilan Muryar Amurka, Sanusi Adamu dake Jahar Adamawan Najeriya da kuma Haruna Mamane bako daga birnin Konni na Jamhuriyar Nijar:

please wait

No media source currently available

0:00 0:05:09 0:00

XS
SM
MD
LG