Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Akwai Ja Akan 'Yar Mata Da Ake Zargin Cewa Wadanda Aka Sace A Chibok Ne


Malam Garba Shehu yace abin yana da daure kai domin hoton yarin yar ya nuna cewa yarinyar bata wuce shekaru tara zuwa goma sha daya

Hukumomin Najeriya da na kasar Kamaru, sun dukufa suna kokarin gudanar da wani cikakken bincike akan mata biyu da aka kama da yunkurin tada bom a kasar Kamaru, batare da yin nasara ba.

Wadanna mata dai ana zargin cewa tana iya kasancewa daga cikin matan da aka sace kimanin shekaru biyu da suka wuce suke wadanda har rana kamar ta yau babau wanilabari.

Kakakin shugaban Najeriya, Malam, Garba Shehu, yace sun sami hotuna na ita yarinya da tace ita tana cikin ‘yan matan daka sace a makarantar garin Chibok.

Amma Malam Garba Shehu yace abin yana da daure kai domin hoton yarin yar ya nuna cewa yarinyar bata wuce shekaru tara zuwa goma sha daya, kuma gashi ‘yan matan da aka sace ‘yan kimanini shekaru goma sha biyar zuwa sha bakwai ne.

please wait

No media source currently available

0:00 0:03:48 0:00
Shiga Kai Tsaye


XS
SM
MD
LG