Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Zaben fidda dan takarar jam'iyar PDP ya bar baya da kura a jihar Kebbi


PDP
PDP

Gwamnan jihar Kebbi alhaji Sa’idu Usman Nasamu Dakingari yace ya zabi Bello Sarkin Yaki a matsayin dan takarar gwamna domin cika alkawarin da ya yi naai kyautatawa al’ummar jihar.

Zaben fitar da gwani a jihar Kebbi ya fuskanci cece kuce da dama tare da korafe korafe da ya sa aka dakatar da shi domin neman masalah,a daga baya kuma aka bayyana sunan Bello Sarkin Yaki wani tsohon soja a matsayin dantakarar jam’iyar PDP a jihar.

A cikin hirarsu da Sashen Hausa. Gwamnan jihar alhaji Sa’idu Usman Nasamu Dakingari yace a lokacin da ya dauki rantsuwa bayan zabensa ya yi alkawarin cewa, zai kyautatawa al’ummar jihar kuma ba zai yi wani abinda zai cutar da suba.

Bisa gacewarshi, dalilin da yasa ya zabi wanda zai gaje shi , shine domin cika alkawarin da yayi cewa, bayan kamala wa’adin mulkinsa zai zabarwa jihar wanda zai gajeshi na kwarai, kuma ya hakikanta cewa Bello Sarkin Yaki shine ya dace da rike wannan mukanin domin ya taka rawar gani a aikinsa an gani.

Wakilinmu Murtala Faruk Sanyinna ya aiko da cikakken rahoton.

Siyasar jihar Kebbi
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:50 0:00
Shiga Kai Tsaye

  • 16x9 Image

    Grace Alheri Abdu

    Grace Alheri Abdu  babbar Edita ce (Managing Editor) a Sashen Hausa na Muryar Amurka wadda ta shafe sama da shekaru 30 tana aikin jarida. Tana da digiri na biyu a fannin dokoki da huldar diplomasiyar kasa da kasa, da kuma digiri na biyu a fannin nazarin addinan al'adun gargadiya na kasashen Afrika.

XS
SM
MD
LG