Kamfanin dillancin labarai na Mauritaniya yace kasar ta mikawa Libya tsohon babban jami’uin leken asiri na marigayi shugaba Muammar Gaddafi, Abdullah al-Sanusi, inda ake sa ran zai gurfana a gaban shari’a.
An kama al-Sanusi a watan Maris a bayan da ya saci jiki ya shiga kasar Mauritaniya bayan da ya batar da kamanni ya kuma yi amfani da fasfo na karya. Tun lokacin, hukumomin Libya sun nemi a mika musu tsohon jami’in leken asirin wanda kotun duniya ma take nema.
Mauritaniya ta nace a kan cewa zata gurfanar da shi gaban shari’a a saboda ya shiga kasar ba tare da izni ba. Amma jami’an gwamnati sun tabbatar cewa al-Sanusi ya bar Mauritaniya yau laraba a cikin wani jirgin saman da ya doshi kasar Libya.
A watan Yuni kotun bin bahasin manyan laifuffuka ta duniya ta bayar da takardar iznin kama al-Sanusi tana mai fadin cewa yana da alhaki, a zaman mai masaniya ko wanda ya bayarda umurnin aikata laifuffuka biyu na cin zarafin bil Adama, ciki har da kisan kai da danniyar siyasa.
An kama al-Sanusi a watan Maris a bayan da ya saci jiki ya shiga kasar Mauritaniya bayan da ya batar da kamanni ya kuma yi amfani da fasfo na karya. Tun lokacin, hukumomin Libya sun nemi a mika musu tsohon jami’in leken asirin wanda kotun duniya ma take nema.
Mauritaniya ta nace a kan cewa zata gurfanar da shi gaban shari’a a saboda ya shiga kasar ba tare da izni ba. Amma jami’an gwamnati sun tabbatar cewa al-Sanusi ya bar Mauritaniya yau laraba a cikin wani jirgin saman da ya doshi kasar Libya.
A watan Yuni kotun bin bahasin manyan laifuffuka ta duniya ta bayar da takardar iznin kama al-Sanusi tana mai fadin cewa yana da alhaki, a zaman mai masaniya ko wanda ya bayarda umurnin aikata laifuffuka biyu na cin zarafin bil Adama, ciki har da kisan kai da danniyar siyasa.