An fara kidaya a kuri’u a Saliyo, bayanda al’umar kasar a jiya Asabar, suka jefa kuri’a, domin zaben sabon shugaban kasa, da wakilan majalisar dokokin kasar.
Wannan ne karo na uku da Saliyo take gudanar da zabe tun bayan kawo karshen yakin basasa a kasar a 2002. Rahotanni sun ce mutane sun dunguma zuwa rumfunan zabe tun da sanyin safiyar jiya Asabar, domin su kada kuri’ar su.
Shugaban tawagar masu aikin sa ido kan zaben na Tarayyar Turai Richard Howitt, ya gayawa manema labarai cewa a safiyar jiyan an gunadar zaben cikin tsanaki, kuma jama’a sun fito sosai.
Hukumar zaben kasar tana da kwanaki 10 daga ranar da aka yi zabe ta bayyana sakamako, idan babu daya daga cikin ‘yan takara tara da suke neman shugabancin kasar da ya sami kashi 55 cikin dari, an ayyana ranar 8 ga watan Disemba, domin a gudanar da zaben fidda gwani.
Shugaban kasar wadda yake kan mulki yanzu, Ernest Bai Koroma, wanda ake yabawa da ayyukan gina kasa, yana fuskantar ‘yan hamayya takwas ciki har da babban abokin takararsa Julius Ma’ada Bio, wanda shine shugaban mulkin sojan kasar na wani dan gajeren lokaci a 1996, kamin ya mika mulki ga gwamnatinn farar hula wacce ita ma bata juma ba.
Kakakin hukumar zaben kasar Albert Massaquoi, ya gayawa MA cewa hukumar ta dauki matakai domin tabbatarda sahihancin zaben da suka hada da horasda ma’aikata. Kuma yace hukumar zata gaggauta bayyana sakamakon zaben fiye da abunda ya faru a baya.
Shugaba Koroma ya sami nasarar zama shugaban kasa, bayan lashe zaben fidda gwani da aka gudanar a 2007. Ahlin yanzu jam’iyyarsa ta APC ce take rike da kujeru mafiya rinjaye a majalisar dokokin kasar.