Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Akalla Mutane 60 Suka Halaka A Abidjan, A bikin Shiga Sabuwar Shekara.


Mutane suke tsaye a gefen kayayyaki na mutane da suka yi turereniya a daren jiya, a Abidjan.
Mutane suke tsaye a gefen kayayyaki na mutane da suka yi turereniya a daren jiya, a Abidjan.
Jami’ai a kasar Cote ‘d Voire sun ce a kalla mutane 60 ne suka mutu bayan da aka sami turereniya a safiyar yau Talata a Abidjan, babban birnin kasar.

Masu agajin gaggawa sunce wasu mutane 200 ne suka jikkata a wanna lamari, wanda ya faru a gundumar da ake kira Flato,wani filin wasa wajenda mutane suka taru domin kallon wasannin kayan wuta na shigar sabuwar shekara.

Tashar talbijin ta AIP a kasar ta bada labarin cewa, galibin wadanda lamarin ya rutsa da su matasa ne. Iyaye wadanda hankalinsu ya tashi sun dunguma zuwa filin wasan domin neman 'yayansu cikin gawarwaki da suke wurin.

Hukumomin kasar sun kaddamar da bincike domin tantance dalilinda ya janyo turereniyar.
Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG