Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Faransa Na Shirin Taimaka Wa Mali


Dakarun Ansar Dine a zaune akan mota a garin Gao dake arewa maso gabashin Mali. June 18, 2012.
Dakarun Ansar Dine a zaune akan mota a garin Gao dake arewa maso gabashin Mali. June 18, 2012.
Shugaban Kasar Faransa Francois Hollande yace a shirye kasarsa ta ke ta dakile kutsen da ‘yan tawaye masu tsatsaurar ra’ayin Islama ke yi a Mali, to amman zai yi hakan ne kawai da amincewar Majalisar Dinkin Duniya.

Mr. Hollande ya fadi a wani jawabin daya yi yau Juma’a cewa kutsen wata tsabar barazana ce ga kasancewar Mali. Ya kara da cewa Faransa za ta ji rokon Mali na neman taimako bisa sharadin da Kwamitin tsaro na Majalisar Dinkin Duniya ya Shinfida.

A jiya Alhamis ne Kwamitin Tsaron yayi wani zama na tattaunawa kan rikicin na Mali, bayan da ‘yan tawaye su ka kama wani muhimmin gari a yunkurin da suke yi zuwa babban birnin kasar ta Kudu. Kwamitin ya bayar da umurnin tura sojojin kasashen waje cikin gaggawa don su dakile wannan matsalar.

Shugaban wuccin gadin Mali Dioncounda Traore ya roki Faransa, wadda ita ta yi wa Mali mulkin mallaka, da ta taimaka masu cikin gaggawa don dakile ‘yan tawayen.
Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG