Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Amurka Ta Koma Gefe A Yunkurin Sasanta Rikicin Sudan Ta Kudu


Amurka ta yanke shawarar karbar wani matsayi na bayan- fage, a yunkurin sasanta rikicin Sudan ta Kudu da ake yi tsakanin gwamnatin kasar da ‘yan tawaye, bayan cikas da aka samu wajen kafa gwamnatin hadaka a tsakanin bangarorin biyu.

A ranar Asabar, gwamnatin Sudan ta Kudu ta ki amincewa wani jirgi dauke da shugaban ‘yan tawaye Riek Machar ya sauka a Juba, babban birnin kasar, bayan da Machar ya bukaci shiga birnin da yawan dakaru da makaman da ba sa cikin matsyar da aka cimma a baya, a cewar Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Amurka, John Kirby.

Kirby ya kara da cewa, lokaci ya yi da bangarorin biyu za su kawar da duk wata matsala da za ta hana kafa gwamnatin hadakar, ta yadda shugaban ‘yan tawayen Riek Machar zai shiga birnin na Juba.

Ya kara da cewa har sai bangarorin biyu sun nuna shirinsu na sasantawa, kafin Amurka ta taimakawa Sudan ta Kudu wajen magance matsalolin tsaro da na tattalin arzikinta.

XS
SM
MD
LG