Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

An Kaddamar Da Shirin Kayata Birnin Maradi


A Jamhuriyar Nijar an kaddamar da shirin kayata birnin Maradi a wani mataki na maida birnin zuwa cikakke birni na zamani.

A Jamhuriyar Nijar, an kaddamar da shirin kayata birnin Maradi a wani yunkuri da gwamnati ke yi na bunkasa biranen kasar.

Wannan wani mataki ne na yin tuni da ranar da jamhuriyar ta Nijar ta zama jamhuriya a karakashin shirin da aka yiwa take da “Maradi Kwalliya.”

“Burin shi ne a kayata wadannan birane a wannan jamhuriya ta bakwai.” In ji Fira Minista Briji Rafini a lokacin da ya ke dasa tubalin kaddamar da shirin.

Shugaban Kwamitin Tsara ayyukan kayata garin na Maradi, Minista Malam Kala Hankarau, ya ce ayyukan da za a gudanar sun shafi gina hanyoyi da filin kwallo da na kokuwa da na wasan kwaikwayo.

A cewar Ministan cikin watanni takwas a ke so a kammal ayyukan wadanda za a yi su na zamani.

Mutane da dama a garin na Maradi sun nuna gamsuwar da wadannan ayyukan da za a fara gudanarwa, sun kuma nuna farin cikinsu.

“Muna masu alfahari da wannan shiri, mun duba mun ga abin da aka yi a birnin Doso.” In ji wani mazaunin garin Maradi.

A shekarar 2013 aka kaddamar da irin wannan aiki a Niamey N’yala, sannan a shekarar 2014 aka kaddamar da na Dosso Soga.

please wait

No media source currently available

0:00 0:02:38 0:00
Shiga Kai Tsaye

Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG