Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

An kai harin bom a garin Suleja na jihar Niger


Harin bom a Najeriya
Harin bom a Najeriya

Rahotanni da muka samu daga garin Suleja na jihar Niger na nuni da cewa, an kai barin bom a wani titin da ake kira Church Road.

Rahotanni da muka samu daga garin Suleja na jihar Niger na nuni da cewa, an kai barin bom a wani titin da ake kira Church Road. Shaidu sun shaidawa Muryar Amurka cewa, mutane hudu sun mutu wasu da dama kuma suka jikkata sai dai bamu tabbatar da wannan adadin daga hukumomi ba. Kawo yanzu babu kungiyar da ta dauki alhakin tada wannan bom din yayinda jami’an tsaro suka isa wurin a domin tantance wadanda abin ya rutsa da su da kuma gudanar da bincike.

XS
SM
MD
LG