Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Ba'a Zaci Samun Karanci Masu Jefa Kuri'a Ba


Ma'aikacin zabe
Ma'aikacin zabe

Rashin fitowar masu kada kuri'a masu yawan ne yasa hukumar zabe kara lokaci.

Anci gaba da bude rumfunan zabe a yau laraba,domin baiwa al’ummar kasar Misra damarsu ta zaben sabon shugaban kasa.

Laraba ce ranar da aka kara domin karfafa gwiwar masu son zuwa rumfunan zabe a dai-dai lokacin jami’an gwamnati ke karfafa gangamin gwiwar da su fita su jefa kuri’arsu a zaben da ake kyautata cewar tsohon jagoran rundunar sojojin kasar Misra Abdul-Fatah el-Siissi ne zai kai ga samu nasara.

Masu fashin baki sun bayyana cewar ba'a zaci samun karancin masu jefa kuri'a a kwanaki biyun farko da aka kebe domin gudanar da zaben ba, hakan ne yasa hukumar zaben kasar tayi karin rana guda,amma duk da hakan ba'a cincirindon masu son kada kuri'a a layin rumfunan zaben a yau ba.

Rashin fitowar masu kada kuri'a masu yawan ne yasa hukumar zabe kara lokaci domin baiwa kowa isasshen lokacin zuwa yin amfani da damarsa ta zaben wanda yake so.
XS
SM
MD
LG