Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Bam ya hallaka mutane 10 a Kamaru


Sojojin Kamaru Na Farautar 'Yan Boko Haram
Sojojin Kamaru Na Farautar 'Yan Boko Haram

Mahukunta a kasar Kamaru sun ce wani bam din kunar bakin wake ya fashe a garin Marwa ya kuma kashe akalla mutane 10 a jiya asabar 24 ga watan Yulin shekarar nan ta 2015.

Wannan harin bam ya zo ne kwanaki 3 da tashin tagwayen bama-baman da akalla mutane 20 suka rasu. Talbijin din gwamnati yace wata mace ce ta tada bam din a wani fitattaccen dandalin dare.

Inda hakan ya ankarar da jami’an soji dana ceto suka shiga neman jikatattu. Kamfanin dillancin labarai na Reuters sun ce sun ji wani babban jami’in soja na cewa akalla mutane guda 60 ne suka jikkata.

Ba dai wanda ya dauki alhakkin wadannan hare-hare, amma hukumomin Kamaru na zargin irin hare-haren ‘yan Boko Haram ne na Najeriya.

XS
SM
MD
LG