Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Britaniya Na Kiran a Cigaba da Yiwa Rasha Barazana


William Hague, ​Ministan harkokin wajen Britaniya
William Hague, ​Ministan harkokin wajen Britaniya

​Ministan harkokin wajen Britaniya, William Hague yace yakamata kasashen turai su cigaba da barazanar nuna karfi da hadin kai, domin mayarwa Rasha martani saboda rigigimun Ukraine.

Hague fa yayi magana ne yau Juma’a kafin ya hadu da ministocin harkokin wajen Tarayyar Turai a birnin Athens, inda ake kyautata zaton daga cikin manyan batutuwan da za’a tattauna shine saka wa Rasha takunkumi.

Hague din yace sojoji dan kadan kawai aka janye daga cikin tarin sojojin da Rasha ta lafta bakin iyakar Ukraine, wanda hakan yake kawo zaman dar-dar, saboda ana tunanin wata zata iya abkawa Ukraine.

Kashashen Turai sun riga sun sakawa Rashan nasu takunkuman, saboda hadewarta da yankin Kirimiya, lamarin da Amurka ta kawayenta suka yiwa kafar ungulu.

Rasha dai ta shiga cikin wannan tsuburi a watan daya wuce, bayan hambare shugaban Ukraine Viktor Yanukovych wanda Rashan take goyawa baya. An hambare shine bayan share makonni jama’a suna zanga-zanga.
XS
SM
MD
LG