Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Cutar Ebola Zata Karu Ninkin -ba-Ninkin a Kasar Liberia


Ma'aikatan kiwon lafiya masu yaki da cutar ebola
Ma'aikatan kiwon lafiya masu yaki da cutar ebola

Alkaluma da hukumar kiwon lafiya ta duniya ta fitar sun nuna cewa cutar ebola na yaduwa a kasashen uku dake yammacin Afirka musamman a kasar Liberia

Adadin mutanen da cutar Ebola ta halaka a yammacin Afirka ya haura zuwa 2,296, Karin mutane 200 cikin kwanaki hudu da suka wuce.

A sabbin alkaluman da hukumar kiwon ta lafiyar ta bayar jiya talata kan annobar tace jimillar mutane dubu 4 da dari uku ne suka kamu da cutar a kasashe biyar da suke yammacin Afirka.

Kusan rabin wannan adadi na mutanen da cutar ta hallaka ko suka kamu da ita duk a Laberiya suke.Rahoton da hukumar ta bayar jiya gameda Laberiya a ciki tayi gargadin cewa cutar “zata rubanya ninkin- ba- ninkin”, kuma tayi harsashen cewa za a ga Karin dubban mutane da zasu kamu da cutar cikin makonni uku masu zuwa.

Haka kuma hukumar kiwon lafiya ta duniyar tace cutar tana kara “yaduwa sosai” a kasashen Guniea da Saliyo.

Ahalinda ake ciki kuma ba’Amurke na hudu da ya kamu da cutar Eobla a yayinda yake aiki a yammacin Afirka ya iso nan Amurka jiya Talata.Mara lafiyar da ba’a bayyana sunansa ko sunanta ba inda zata ko zai ci gaba da jinya, kamar takwarorinsa da suka gabata.

XS
SM
MD
LG