Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Dalilin Hasarar Mulkin PDP ya Wuce Maganar Kudi


PDP
PDP

Shugaban kwamitin gano bakin zaren dalilin faduwar jami'iyyar PDP a zaben da ya gabata, sanata Ike Ikweremadu, ya ce zai yi aiki tukuru wajen jagoranci kwamitin don samar da mafita ta hanyar farfado da jami'iyyar ta PDP don taka rawar gani a zabe mai zuwa a 2019.

Sanata Ikweremadu, ya furta haka ne a lokacin kaddamar da kwamitin a hedkwatar jami'iyyar a Wadata plaza. Kan gaba a kalubalen da kwamitin zai duba shine zargin handame Biliyoyin Naira da shuwagabanin jami'iyyar suka yi da sauran hainci na masu ruwa da tsaki haka da Angulu da kan Zabo a wasu sassa.

Adamu Maina Waziri wanda yanke mukaddashi sakataren kwamitin, yace " inda kana so ka jeho fittina a cikin al'uma a wannan zamani masamma a kasar mu Najeriya shine ka kawo maganar kudi mu muna ganin abun da ya kawo mana hasarar mulki ba maganar kudi bane abubuwan ya wuce kudi zamuyi abun da zamuyi don mu sake farfado da jami'iyya don ta zauna da kafar ta ginu da kuma yin hamayya da fatan sake karbar mulki a zaben 2019."

please wait

No media source currently available

0:00 0:02:36 0:00

Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG