Wakiliyar Sashin Hausa Zainab Babaji ta bada rohoton cewa “al’umar Fulani sun koka matuka akan bullar wata cuta da ke shafar huhun dabbobi kuma lamarin yayi sanadiyyar mutuwar dubban shanu a Najeriya”.
Sakataren kungiyar miyatti Allah “cattle breeders” na jahar Nasarawan Najeriya wato Mohammadu Hussaini yace “cibiyar samar da rigakafi da magungunan dabbbobi da ke VOM a jahar Filato ce keda alhakin samar masu da magungunan.
Amma a halin da ake ciki yanzu shine makiyayan na ketarawa zuwa kasar kamaru ne kafin su samo wannan magani a cewar sakataren kungiyar, kuma hakan ya sa Fulani da dama asarar dabbobinsu, “ya ce fiye da shanu dubu uku su ka mutu cikin dan kankanin lokaci”.