Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Gara In Kashe Kaina Da A Tasa Keyata Zuwa Amurka- Kashamu


Zababben dan majalisar dattijai daga jihar Ogun Buruji Kashamu yace gara ya kashe kansa da ya bari a tasa keyarsa zuwa Amurka domin amsa laifin safarar hodar Ibilis.

Wata kotun tarayya a Lagos tace hukumar NDLEA mai yaki da safara da kuma shan muggan kwayoyi tana da hurumin kama zababben dan majalisar dattijai daga jihar Ogun Buruji Kashamu, tare da furfanar da shi a gaban kuliya.

Sai dai alkalin kotun Ibrahim Buba yace hukumar tayi riga malam masallaciu da ta yiwa gidan dan majalisar kawanya kafin samun izinin kotu.

A cikin hirarsu da wakilinmu Babangida Jibril, shugaban hukumar Ahmed Giade ya bayyana cewa, sun killace gidan ne,sabili da akwai bukatar da gwamatin Amurka ta gabatar ga gwamatin Najeriya tana bukatar a mika shi ga gwamnatin Amurka, bisa tuhumarshi da Amurka ke yi da safarar hodar ibilis, da ya yi zuwa Amurka.

Shugaban hukumar NDLEA ya bayyana cewa, basu sami kama Mr. Kashamu ba sabili da ya kulle kansa a bandaki, ya kuma ce gara ya kashe kansa da a kama shi a tasa keyarsa zuwa Amurka.

Ga cikakken rahoton.

Gara In Kashe Kaina Da A Tasa Keyata Zuwa Amurka- Kashamu - 2'25"
please wait

No media source currently available

0:00 0:02:25 0:00
Shiga Kai Tsaye

  • 16x9 Image

    Grace Alheri Abdu

    Grace Alheri Abdu  babbar Edita ce (Managing Editor) a Sashen Hausa na Muryar Amurka wadda ta shafe sama da shekaru 30 tana aikin jarida. Tana da digiri na biyu a fannin dokoki da huldar diplomasiyar kasa da kasa, da kuma digiri na biyu a fannin nazarin addinan al'adun gargadiya na kasashen Afrika.

XS
SM
MD
LG