Daga bara zuwa yanzu sama da makarantu 120 masu zaman kansu gwamnatin jihar Neja ta rufe saboda kasawarsu na cika kai'idodin da aka gindiya masu.
Darakta a ma'aikatar ilimi ta jihar Malam Isa Jibril yace an dauki matakan ne saboda basu cika ka'idojin da aka basu ba kafin su bude makarantun.
Malam Zuberu S.D. na Kwalajin Sudan dake Kontagora yace kafin a yadda mutum ya bude makaranta sai masu sa ido sun ga wurin sun kuma amince.
Saidai kungiyar masu makarantu dake zaman kansu sun ce sun gamsu da tanadin da suka yiwa makarantunsu.
Alhaji Danladi Kowa shugaban makarantar Kowa dake Minna babban birnin jihar, kuma shugaban kungiyar masu makarantun dake zaman kansu yace sun amince da matakan da gwamnati ta dauka saboda da zara mutum ya samu cancanta gwamnati zata bada goyon baya.
Wasu makarantun basu cancanta ba. Wasu ma sun fara ne a cikin shaguna abun da bai kamata ba.
Malam Idris Adarawa na Kwalajin Sudan yace kara sawa malamai idanu zai yi tasiri a makarantu masu zaman kansu. A tabbatar an samu kayan aiki isassu da kuma hadin kan jama'a.
Ga rahoton Mustapha Nasiru Batsari.