Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Har Yanzu Babu Adadin Wadanda Aka Kashe a Harin Kano


Har yanzu hukumomi ba su bayyana adadin mutanen da suka mutu ko wadanda suka jikkata a hare-haren bama-bamai da aka kai a Babban Masallacin Jumma'a na Kano jiya ba.

Har yanzu hukumomi ba su bayyana adadin mutanen da suka mutu ko wadanda suka jikkata a hare-haren bama-bamai da aka kai a Babban Masallacin Jumma'a na Kano jiya ba.

Wakilan Muryar Amurka, Mohammed Salisu Rabi'u da Mahmud Ibrahim Kwari, sun tattauna kai tsaye ta www.dandalinvoa.com inda suka bayyana cewa watakila ma zai yi wuya a iya sanin adadin wadanda suka mutu.

Sai dai kuma ba a takaita zirga-zirgar mutane a cikin birnin na Kano ba, yayin da hukumomin asibiti suka roki jama'a masu hali da su kai gudumawar jini domnin ceto rayukan wadanda suka ji rauni ainun, suka kuma yi hasarar jini a manyan asibitocin da suke birnin.

Ga cikakken bayanin tattaunawar:

Tattaunawa Kai Tsaye da Wakilanmu na Kano a Safiyar Asabar - 11'15"
please wait

No media source currently available

0:00 0:11:15 0:00
Shiga Kai Tsaye

XS
SM
MD
LG