Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Hukuncin Simone Gbagbo Ya Haifar da Kiyayya


Tsohon shugaban Ivory Coast Laurent Gbagbo (hagu) da matarsa Simone Gbagbo a zaune (dama) a lokacin da ake musu shari'a
Tsohon shugaban Ivory Coast Laurent Gbagbo (hagu) da matarsa Simone Gbagbo a zaune (dama) a lokacin da ake musu shari'a

Wani tasiri da hukuncin daurin shekaru 20 da wata kotu ta yi wa tsohuwar matar shugaban Ivory Coast shi ne zai zama darasi ga sauran shugabannin, sai dai a wani bangaren masu sharhi na cewa hukuncin ya farfado da kiyayyar da ke tsakanin magoya bayan Laurent Gbagbo da na shugaba Alassane Ouattara.

Tun bayan da aka yankewa matar tsohon shugaban kasar Ivory coast hukuncin zaman gidan yari na tsawon shekaru mutane daga bagarori daban-daban na ci gaba da tsokaci kan wannan hukunci.

A ranar Talatar da ta gabatab wata kotu ta samu Simone Gbagbo da laifin tunzura rikicin da ya biyo bayan zaben shekarar 2010, lamarin da ya yi sanadiyar mutuwar mutane sama da 3,000.

Sai dai wasu masu sharhi na cewa duk da hukuncin ya yi dai dai zai iya farfado da kiyayya tsakanin magoya bayan tsohon Shugaba Laurent Gbagbo da magoya bayan Alassane Ouattara.

“Lallai wannan hukunci ya hada hayaniya tsakanin tsohon shugaba Gbagbo da sabon shugaba, saboda sun gwada cewa hukuncin ya yi tsauri ya yi yawa” In ji Usman Jah Ustaz, wani dan jarida a Ivory Coast.

Sai dai mai sharhin ya ce hukuncin zai iya zama darasi ga sauran matan shugabannin kasar domin wannan shi ne karo na farko da aka taba yanke wannan hukunci a wata da ta taba irin wannan mukami.

please wait

No media source currently available

0:00 0:02:56 0:00
Shiga Kai Tsaye

XS
SM
MD
LG