Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

APC ta Yiwa Daliban Cibok Addu'a


APC
APC

Yayin da take taron kawo karshen wa'adin shugabannin riko na jihar Sokoto, jam'iyyar APC ta bude taron ne da ta musamman ma daliban da awasu 'yan bindiga suka sace a Chibok dake jihar Borno.

Jam'iyyar APC ta yi taro a Sokoto domin kawo karshen wa'adin shugabannin riko biyo bayan nadin da jam'iyyar ta yi.

Amma taron ya kasance tamkar taron yiwa daliban da wasu 'yan bindiga suka sace ne addu'a ta musamman ganin tsawon lokacin da malamai suka kwashe suna addu'a. An gudanar da addu'o'in ne domin samun mafita ga daliban da aka sace a garin Chibok na jihar Borno. Haka kuma malaman sun yi addu'ar samun masalahar Ubangiji ga jama'a da jihohin dake fama da hare-hare a arewacin kasar.

Zaben shugabannin APC a jihar Sokoto ya kasance ta hanyar sasantawa ne inda Bala Abubakar ya zama sabon shugaban jam'iyyar na jihar. Duk da sukar da jama'a keyi na hana yin zaben fitar da shugabanni, gwamnan jihar Aliyu Magatakarda Wamako na ganin itace hanya mafi sauki a kokarin magance rarrabuwar kawuna.

A jihar Zamfara ma bata sake zani ba. Shugaban rikon kwarya Lawali Makaman Kaura jam'iyyar tace shi ya zama tabbatacen shugaban jam'iyyar na jihar lamarin da ya sa wasu suna korafin an hanasu tsayawa takara karfi da yaji kamar irinsu Mohammed Dole. Yace ya je har Abuja ofishin jam'iyyar inda ya biya kudi ya yanki takardar shiga takara amma abun mamaki sai jam'iyyar ta gabatarda Lawali a matsayin shugaban jihar.

Ga karin bayani.
please wait

No media source currently available

0:00 0:02:53 0:00
Shiga Kai Tsaye
Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG