Jami’ai a Pakistan sunce wani hari daga jirgin sama mara matuki ya kashe mutane 8 da ake zargi mayakan sa kai ne, a kusa da iyakar kasar da Afghanistan, yankin da ake zato na karkashin ikon Taliban.
Jami’ai sunce ana kyautata zaton akwai wani kusan al-Qaida a cikin wadanda harin ya kashe a kusa garin Mir Ali, a arewacin Waziristan.
Harin da aka kai a safiyar talata na daya daga cikin hare-hare na baya-bayan nan da aka kai a fadin wannan yanki. Ranar lahadi da ta gabata, jami’an Pakistan sunce wasu mutane guda 9 da ake zaton mayakan Taliban ne suka halaka daga harin da jiragen yaki da basu da matuka a ciki, a wata mafakarsu, a kudancin Wziristan.
Gwamnatin Pakistan ta fito fili tayi Allah wadai da harin da wadannan jirage suke kaiwa a matsayin keta diyaucin kasar, amma ana kyautata zaton akwai taimakon ma’aikatar leken asirin Pakistan wajen kai wadannan hare-hare.
Jami’ai sunce ana kyautata zaton akwai wani kusan al-Qaida a cikin wadanda harin ya kashe a kusa garin Mir Ali, a arewacin Waziristan.
Harin da aka kai a safiyar talata na daya daga cikin hare-hare na baya-bayan nan da aka kai a fadin wannan yanki. Ranar lahadi da ta gabata, jami’an Pakistan sunce wasu mutane guda 9 da ake zaton mayakan Taliban ne suka halaka daga harin da jiragen yaki da basu da matuka a ciki, a wata mafakarsu, a kudancin Wziristan.
Gwamnatin Pakistan ta fito fili tayi Allah wadai da harin da wadannan jirage suke kaiwa a matsayin keta diyaucin kasar, amma ana kyautata zaton akwai taimakon ma’aikatar leken asirin Pakistan wajen kai wadannan hare-hare.