Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Kasar Nijer Na Taron Tsara Manufofin Kare Kai Daga Rigingimu


Nijer ta kasance a tsakiyar kasashe uku masu fama da tashin hankali da rashin zaman lafiya wato Najeriya da Mali da kuma Libiya
Nijer ta kasance a tsakiyar kasashe uku masu fama da tashin hankali da rashin zaman lafiya wato Najeriya da Mali da kuma Libiya

Majalisar Dinkin Duniya da Hukumar Koli mai neman dawwamar da zaman lafiya a Nijer ne suka shirya taron

Wasu kwararru daga yankuna daban-daban na kasar Jamahuriyar Nijer na gudanar da wani taron binciko dalilan dake haifar da fitintinu da tashe-tashen hankula tsakanin al'ummar kasar domin a samar da hanyar magance su.

please wait

No media source currently available

0:00 0:03:11 0:00
Shiga Kai Tsaye

Hukumar raya karkara ta Majalisar Dinkin Duniya, UNDP, da Hukumar Koli mai Fafutukar Dawwamar da Zaman Lafiya a Nijer ne suka hada guiwa su na gudanar da taron da nufin tsara wani kundin da hukumomin kasar Nijer zasu yi amfani da shi su yi rigakafin afkuwar rigingimu a kasar, musamman ma idan aka yi la'akari da cewa kasar ta Nijer na zagaye da kasashen dake fama da karancin zaman lafiya da kwanciyar hankali.

Wakilin Sashen Hausa a birnin Niamey Abdoulaye Mamamne Amadou ne ya hada rahoton kuma ya aiko.

Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG