Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Kotun kolin Najeriya ta tabbatar da zaben gwamnan Taraba


Sanata Aisha Jummai Alhassan da kotun koli ta yi watsi da kararta
Sanata Aisha Jummai Alhassan da kotun koli ta yi watsi da kararta

Kotun kolin Najeriya ta yi watsi da karar Aisha Alhassan 'yar takarar kujerar gwamnan jihar Taraba

Alkalin kotun kolinya amince da hukuncin kotun daukaka kara da tun can baya ya tabbatar da zaben Dickson Isyaku a matsayin gwamnan jihar Taraba.

Alkalan su bakwai duk sun yi watsi da karar da Sanata Aisha Alhassan ta shigar biyo bayan hukuncin kotun daukaka kara.

Shugaban jam'iyyar APC na jihar Taraba Alhaji Jika Ardo da yake mayarda martani akan hukuncin yace a matsayinsa na wanda ya dogara ga Allah ya yadda da duk hukuncin da kotun ta yanke. Saboda ko ma yace mai yadda ba ina mutum zashi domin daga hukuncin kotun koli sai dai Allah. Kara kara da ba magoya bayansu hakuri tare da jijina masu dangane da irin goyon bayan da suka basu.

Abubakar Bawa mai ba gwamnan shawara kan harkokin siyasa yace sun godewa Allah saboda gaskiya daya ce.

Ga karin bayani.

please wait

No media source currently available

0:00 0:02:07 0:00

XS
SM
MD
LG