Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Malam Dudu Rahama a Taron Gamayyar Jam'iyyun Adawa


Gamayyar jam’iyyun siyasa ta jihar Maradi da ake kira (ARDR) A janhuriyar Niger, sunyi wani taron manema labarai

Malam Dudu Rahama, shugaban kungiyar hadakar jam’iyyun jihar Maradi, ya karfafa guywar magoya baya da kuma yin kira a garesu da su tashi tsaye don zaben dake tafe.

Da shike an fara shirye-shiryen zaben shekara mai zuwa (2016) a janhuriyar Niger, Malam Dudu yace yana da muhimmanci su yi wa jama’a tuni cewa lokaci yayi da zasu tashi tsaye don ganin sun kawarda jam’iyyar adawa ta PNDS Tarayya amma kuma ya zama dole su wayar wa magoya bayansu kai.

Ya kara da cewa siyasar da suke yi ta dimokradiyya ce, ta neman mulki, ta jefa kuri’a kuma. Saboda haka ya zama wajibi su yi wa magoya bayansu bayani bisaga dokar demokradiyya, akan abinda suke ciki don warware duk wani rudani.

please wait

No media source currently available

0:00 0:01:26 0:00

XS
SM
MD
LG