Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Mun Shirya Tsaf Inji AIG Usman


'yan Sandan Najeriya
'yan Sandan Najeriya

Rundunar ‘yan sandan Najeriya ta ce ta shirya tsaf domin ganin cewa an gudanar da zaben gwamnoni da za’a sake gudanarwa a jahohin biyu na Abiya da Imo, a sakamakon matsalolin da aka fuskanta a zaben da ya gabata.

Rundunar ‘yan sandan Najeriya ta ce ta shirya tsaf domin ganin cewa an gudanar da zaben gwamnoni da za’a sake gudanarwa a jahohin biyu na Abiya da Imo, a sakamakon matsalolin da aka fuskanta a zaben da ya gabata.

Babban jami’in ‘yan sanda mai kula da shiyya ta tara kuma mai mataimakin babban sufeton ‘yan sandan Najeriya AIG Usman A Gwari a hirar su da Lamido Abubakar Sokoto ya bada tabbacin cewar a shirye suke domin tabbatar da tsaro dakuma bin doka da oda a wadan nan wurare.

Jami’in tsaron yayi Karin bayani kamar haka “rundunar ‘yan sanda ta shirya domin gudanar da wannan zabe da za ayi gobe asabar a wasu kananan hukumomin wadan nan jahohi guda 9, kuma akwai isassun jami’an tsaron da suka hada da ‘yan sanda, sojoji, civil defens da sojojin ruwa da sauran su”.

Zabe a wadannan kana nan hukumomin y azo da matsala ne yayin da aka sami sace sacen na’urar tantance katunan zaben da kuma akwatunan zaben wanda hakan ya haifar da rudani a wasu yankunan jahohin kuma yayi sanadiyyar soke zaben.

Hukumar zaben jahar Abiya ta ce tariga ta rarraba kayan aiki a sassa daban daban haka ita ma takwarar ta ta jahar imo tace ta riga ta kammala raba wadan nan kayan aiki.

Mun Shirya Tsaf Inji AIG Usman - 2'07"
please wait

No media source currently available

0:00 0:02:07 0:00
Shiga Kai Tsaye

XS
SM
MD
LG