Jama’a da dama na ci gaba da kauracewa jihohin da aka kafa dokar-ta-baci zuwa wadansu jihohi da kuma kashe dake makwabta.
Rahotanni na nuni da cewa, mutanen da suke tafiya gudun hijira sun bayyana cewa, ya zama dole su kauracewa matsugunansu domin rashin kayan masarufi da muhimman ababan jin dadin rayuwa.
Sun kuma bayyana cewa, banda yunwa, suna zaune a cikin tashin hankali. Wadansu daga cikin ‘yan gudun hijiran da suka isa Gombe daga Maiduguri da wakilinmu Abdulwahab Mohammed ya yi hira da su sun bayyana irin halin da suka shiga kafin suka isa garin Gombe.
Rahotanni na nuni da cewa, mutanen da suke tafiya gudun hijira sun bayyana cewa, ya zama dole su kauracewa matsugunansu domin rashin kayan masarufi da muhimman ababan jin dadin rayuwa.
Sun kuma bayyana cewa, banda yunwa, suna zaune a cikin tashin hankali. Wadansu daga cikin ‘yan gudun hijiran da suka isa Gombe daga Maiduguri da wakilinmu Abdulwahab Mohammed ya yi hira da su sun bayyana irin halin da suka shiga kafin suka isa garin Gombe.
-
Grace Alheri Abdu
Grace Alheri Abdu babbar Edita ce (Managing Editor) a Sashen Hausa na Muryar Amurka wadda ta shafe sama da shekaru 30 tana aikin jarida. Tana da digiri na biyu a fannin dokoki da huldar diplomasiyar kasa da kasa, da kuma digiri na biyu a fannin nazarin addinan al'adun gargadiya na kasashen Afrika.