Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

RAHOTO NA MUSAMMAN A KAN BOKO HARAM: Jini, Hawaye da Fargaba a Daular El-Kanemi - 'Dulmuyar Najeriya, Dulmuyar Afirka ta Yamma' (Babi na 5)


Manyan jami’an Jihar Zamfara a wurin jana’izar wasu mutane su fiye da 100 wadanda ‘yan bindiga suka kashe a wani harin watan Afrilu. (VOA/Murtala Farouk)
Manyan jami’an Jihar Zamfara a wurin jana’izar wasu mutane su fiye da 100 wadanda ‘yan bindiga suka kashe a wani harin watan Afrilu. (VOA/Murtala Farouk)

Kashe-kashe da zub da jini da tashe-tashen hankula sun zamo ruwan dare a yankin arewa maso gabashin Najeriya a dalilin hare-haren ‘yan Boko Haram. A yayin da wannan tashin hankali ke bazuwa zuwa wasu sassan na Najeriya, har ma da makwabtanta, fargaba tana kara yawaita cewa watakila gwamnatin Najeriya ba ta san yadda zata takali wannan batu ba. Ko kuma tana kara rura wutar fitinar ne ma da kanta.

A yanzu dai, duk da ayyana Daular Islama da Boko Haram ta yi a Gwoza da wasu yankunan da ta kwace a kusa da nan, babu wanda yake ganin cewa zata iya rusa Najeriya.

Abinda ake kara damuwa a kai shi ne hanyoyin da kungiyar take samun kudaden gudanar da ayyukanta, da yadda take iya kwace yanki mai fadi, musamman a kusa da bakin iyakoki inda babu tsaro sosai. A wannan yankin dake cike da kasashe masu fama da fitina, kamar Mali, Chadi, Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya, da ma kasashe kamar Nijar, take-taken Boko Haram sun sanya ta cikin jerin kungiyoyi masu hatsarin gaske.

Pham yace, “A bayan kai hare-haren da ta keyi a kasashe makwabtan Najeriya, Boko Haram ta haddasa rashin kwanciyar hankali a kasashen da ba su da karfin da zasu iya yakarta.”

A cikin ‘yan makonnin da suka biyo bayan sace dalibai mata na Chibok a watan Afrilu, gwamnatin shugaba Goodluck Jonathan ta yi watsi da tayin kasashe irinsu Amurka, Turai da wasunsu na taimakawa wajen bin sawun daliban. Amma kuma a saboda yadda duniya ta nuna fusata, gwamnatin Najeriya ta mika kai. A watan Mayu, sojojin sama na Amurka da aka girka a Chadi sun fara amfani da jiragen sama marasa matuka a ciki tare da wani jirgin leken asiri na musamman.

A watan Nuwambar 2013, ma’aikatar harkokin wajen Amurka ta ayyana Boko Haram a zaman kungiyar ta’addanci, ayyanawar da manufarta ita ce toshe hanyoyin samun kudaden gudanar da ayyukanta.

Amma kuma, Amurka ta bayyana damuwa a kan yadda dakarun tsaron Najeriya suke keta hakkin bil Adama. A shekarar 2012, a karkashin wata doka da aka fi sani da sunan “Leahy Amendment” wadda ta haramtawa Amurka bayar da taimako ga wata rundunar sojan kasar waje da aka samu tana keta hakki, ma’aikatar harkokin wajen Amurka ta ki yarda ta tallafa da kudi wajen horas da wasu sojojin Najeriya su 211. Haka kuma, an ce an takaita bayarda agajin Amurka ga wata bataliyar sojojin Najeriya da aka tura kasar Mali domin yakar ‘yan ta’adda masu alaka da kungiyar al-Qa’ida.

Hare-haren da 'yan Boko Haram ke kaiwa a yanzu, ya zarce yankin arewa maso gabashin Najeriya zuwa wasu sassan, kamar wannan jerin kantuna dake Abuja, babban birnin kasar, inda aka kai hari ranar 25 ga watan Yuni, 2014. (Reuters)

Abinda babu tabbas shi ne ko gwamnatin shugaba Jonathan tana da sha’awa ko kuma bukatar sake dabarun yadda take tinkarar wannan lamari na Boko Haram. A ranar 22 Yuli, ‘yan Boko Haram sun lalata wata gadar da ake bi zuwa Kamaru, suka kara karya harkar kasuwanci dake zuwa ko fita daga Maiduguri. Kwana biyu bayan wannan, gwamnatin Najeriya ta bayyana cewa ita da Kamaru da Chadi da kuma Nijar zasu kafa wata rundunar yanki mai sojoji dubu 2 da 800 domin yakar tsageran.

A saboda bacin rai kan yadda al’amura suka tabarbare, da yadda gwamnatin Najeriya ta kasa tabuka wani abin a zo a gani, matasan cikin Maiduguri sun yi kukan kura, suka fara kakkafa kungiyoyin banga da ake kira ‘Yan Gora ko kuma Civilian-JTF, domin kare unguwanninsu.

Jami’ai sun yi na’am da cewa wadannan ‘Yan Gora dake dauke da sanduna, adduna, kwari da baka, sun taimaka wajen fatattakar ‘yan Boko Haram daga cikin babban birnin. Amma kungiyoyin kare hakki sun ce wadannan ‘yan banga su na da hannu wajen cin zarafi da azabtar da wadanda ake zaton ‘yan Boko Haram ne.

A garin Mainok, dake kudu da Maiduguri a kan hanyar zuwa Damaturu, sau uku ‘yan Boko Haram su na kai farmaki tare da kona makarantar sakandare ta garin tun 2012. A bayan hari na baya-bayan nan, gwamna Kashim Shettima na Jihar Borno, yayi tattaki zuwa makarantar inda ya lashi takobin sake gina wannan makaranta, tare da karfafawa mutanen garin guiwa.

Sa’o’i biyu kacal a bayan da ya bar garin, sai ‘yan Boko Haram suka komo suka kona sauran gidajen dake tsaye.

“Zamu sake gina wannan makaranta, ko da sau dubu ne ma,” in ji gwamna Shettima a lokacin da yake magana da VOA. “Wadannan mutane ne da suka ce bai kamata muje makarantar Boko ba. Idan ba mu gina wannan makaranta ba, ai sun samu nasara ke nan a kanmu. Idan kuma muka kyale su suka cimma burinsu, mun shiga uku.”

Karin Bayani akan Jini, Hawaye da Fargaba a Daular El-Kanemi >>

Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG