Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

RAHOTO NA MUSAMMAN A KAN BOKO HARAM: Jini, Hawaye da Fargaba a Daular El-Kanemi - 'Hanyar Soja Ce' (Babi na 4)


Babban masallacin garin Gombe, garin da dubban ‘yan gudun hijirar dake tserewa hare-haren Boko Haram a jihohin Borno da Yobe, suka maida gida a yanzu. (VOA/Ibrahim Ahmed)
Babban masallacin garin Gombe, garin da dubban ‘yan gudun hijirar dake tserewa hare-haren Boko Haram a jihohin Borno da Yobe, suka maida gida a yanzu. (VOA/Ibrahim Ahmed)

Kashe-kashe da zub da jini da tashe-tashen hankula sun zamo ruwan dare a yankin arewa maso gabashin Najeriya a dalilin hare-haren ‘yan Boko Haram. A yayin da wannan tashin hankali ke bazuwa zuwa wasu sassan na Najeriya, har ma da makwabtanta, fargaba tana kara yawaita cewa watakila gwamnatin Najeriya ba ta san yadda zata takali wannan batu ba. Ko kuma tana kara rura wutar fitinar ne ma da kanta.

A saboda yadda tashin hankalin Boko Haram yayi tsanani, shugaba Goodluck Jonathan na Najeriya ya kafa dokar-ta-baci a Borno da wasu jihohi biyu makwabtanta a watan Mayun 2013.

A yayin da aka ga alamun tsagera sun fara fin karfin sojoji da ‘yan sanda sai aka kafa rundunar tsaro ta hadin guiwa, JTF, domin yakar ‘yan Boko Haram gadan-gadan. Rundunar ta girka dubban ‘yan sanda da sojoji a kewayen Borno inda suka kafa wuraren binciken ababen hawa da mutane, da yin sintiri tare da kai sumame. A bara, an kafa sabuwar shiyya ta rundunar sojoji da ake kira Shiyya ta 7, aka kafa hedkwatarta a Maiduguri.

Amma kuma, akwai tababar ko hukumomin tsaron Najeriya zasu iya shawo kan matsalolin shugabanci da kuma zarmiya da cin hancin da suka zamo ruwan dare, domin su samu sukunin kawo karshen wannan fitina.

Wani tsohon jakadan Amurka a Najeriya, Robin Sanders, ya fadawa wani zaman sauraron shaida na majalisar wakilan Amurka a ranar 11 ga watan Yuni, cewa “sojojin Najeriya na yanzu ba su taba fuskantar wani abu makamancin abinda suke fuskanta yanzu a hannun Boko Haram ba.” Ya kara da cewa, “Najeriya ta fada cikin yaki ko rikici na dogon lokaci, kuma dole ta fahimci hakan. Wannan ba fitina ce da ta shafi yanki guda kawai ba.”

A cikin wasu hirarraki masu yawa da suka yi da VOA a watannin Afrilu da Mayu a Borno da wasu wuraren, jami’an ‘yan sanda, da sojoji da jami’an gwamnati sun yi kuka da cewa zarmiya da cin hanci sune suke nakkasa kokarin yakar Boko Haram tare da kashe kwarin guiwar dakaru. Sojoji suka ce a lokuta da dama ana tura su bakin daga ba tare da an biya su kudaden alawus nasu ba. Wani soja yace an tura su suka yi kwanaki uku a cikin daji, amma kuma Naira dubu daya kacal aka ba kowannensu. Kananan ‘yan sanda da sojoji duka sun yi korafin cewa manyansu ne ke cika aljifansu da kudaden alawus din nasu tare da wadanda ake warewa don sayen makamai.

Wani dan sanda Mobayil da yace a kira shi da sunan Malo kawai, ya bayyana cewa “abin kunya ne Najeriya ta ce zata gayyaci kasashen waje suzo su mata wannan yaki. Muna da makaman da zamu iya yin wannan yaki, amma an hana mu. Da hannayenmu zamu yake su?”

Wani bam da aka boye cikin mota ya tashi kusa da wata kasuwa ran 2 Yuli, 2014, a Maiduguri, ya kashe mutane akalla 56. Jami'ai suka ce akasarin wadanda suka mutu, mata ne tsoffi dake sayar da gyada da ruwa ko lemo a kasuwar. (AP)

A watan Mayu, wasu sojoji sun bude wuta a kan motar babban kwamandan shiyya ta 7, wanda suka zarga da laifin kyale ‘yan’uwansu suka mutu a hannun Boko Haram. Wasu sojojin ma sun ce akwai sojan Najeriya dake yaki ma Boko Haram. Wani soja, ya bayyanawa VOA labarin abinda ya faru lokacin wani fada a watan Mayu a Borno, inda ya gane wani daga cikin mayakan Boko Haram.

“Mun sansu,” in ji shi “domin kuwa wasu daga cikinsu sune suka koya mana yadda ake yaki da ta’addanci. Wasu daga cikin Boko Haram da muke yaka sojojin Najeriya ne da suka horas da mu.”

Alhaji Rijiya Bama, na kungiyar ‘yan kasuwa ta Jihar borno, yace kwanakin baya ya fito daga Bama za shi Maiduguri, ya ga wani abin al’ajabi a kauyen Kawuri a lokacin da yara ‘yan bindiga na Boko Haram suka koro wani a mota har zuwa inda sojoji suka kafa shingen bincike. Sun zo suka harbe mutumin, sojoji su na kallonsu, amma ba suyi komai ba. Sai daga baya suke fadawa masu motocin dake tsaye a wurin cewa ba a ba su umurnin su yi harbi ba sai idan an kai musu hari.

Sannan kuma sai batun wani bidiyon da aka dauka da wayar salula, daya daga cikin wasu fayafayen bidiyo guda hudu da wannan sojan ya ba VOA a bayan da ya bayyana abinda ya kira “Hanyar Soja” (The Military Way) ta kawo karshen wannan fitinar ‘yan Boko Haram.

Yadda a ke Kashe Yan Boko Haram
please wait

No media source currently available

0:00 0:01:43 0:00

Wannan bidiyo na minti biyu, wanda kididdiga ta nuna cewa an dauke shi a ranar 26 Mayu, 2014, ya kunshi yadda wasu mutanen da aka ga alamun cewa sojojin Najeriya ne, suke yanka mutane akalla hudu. A cikin wannan bidiyon, sojojin ne suke bada umurnin yadda ake yanka mutanen. Masu sanye da kayan soja da kansu suka yanka biyu daga cikin mutanen, yayin da wasu mutanen biyu sanye da kayan farar hula suke rike da wadanda ake yankawa a bakin wani katon rami da aka tona ana tura gawarwakin wadanda aka yanka ciki. An umurci wani sanye da kayan farar hula, a kan yazo ya yanka guda daga cikin mutanen, kuma an ga alamu a fuska da jikinsa kamar bai so yin hakan ba.

Sojojin dake cikin wannan bidiyo sun yi ta maganganu da harshen Turancin Burokin (Pidgin) irin wanda a Najeriya kadai ake yinsa, ya bambanta da na kasashe irinsu Ghana da Liberiya da Saliyo,sannan kuma su na hadawa da harshen Hausa. Wannan ya bambanta da maganganun ‘yan Boko Haram da aka saba gani ana ji a hotunansu na bidiyo inda suke magana da Hausa, amma Hausa irin ta Kanuri. Mutanen da aka yanka dai ba a ji sun ce komai a wannan bidiyo ba.

Sojan da ya bada VOA wannan bidiyo, yana aiki ne a karkashin Shiyya ta 7 (7th DIV) ta rundunar sojojin Najeriya, kuma ya mika shi ne lokacin wata ganawa a wani sansanin soja cikin jihar Borno bisa sharadin cewa ba za a fadi inda aka yi wannan ganawa ko kuma sunansa ba. VOA dai ba ta iya tabbatar da sahihancin wannan bidiyo dari bisa dari ba, amma kuma ta sanya kwararru sun binciki asalinsa, da harsunan sojojin da ke cikin bidiyon, da dabi’unsu, da irin makaman da suke rike da su, da kuma yanayin wurin da aka dauki wannan bidiyo. Har ila yau wani kwararre a wajen VOA guda daya shi ma ya nazarci wannan bidiyo ya kuma furta cewa da alamun na zahiri ne. Ita ma kungiyar kare hakkin bil Adama ta Amnesty International ta wallafa sassan wani bidiyon da yayi kama da wannan, amma kuma wanda aka dauka da wata kyamara dabam daga wani gefen dabam.

A lokacin da yake bayani a kan wannan da sauran bidiyon da ya ba VOA dake nuna yadda ake daure wadanda ake tuhuma ana musu tambayoyi, ko gana musu azaba, sojan yace “wadannan ‘yan Boko Haram marasa imani, muna magance su ta Hanyar Soja ne.” Da aka tambaye shi ko mecece “Hanyar Soja” sai yace ba zaka so ka sani ba. “Mu dai ba mu son kashe wanda bai ji ba, bai gani ba.”

Yace yawancin ‘yan Boko Haram da ake gani din nan, ba su ne mayakan kungiyar na zahiri ba, ainihin ‘yan Boko Haram din daga baya suke fitowa sanye da bakaken kaya.

“An ba wadannan mayakan Boko Haram da kake gani wani abu ya sauya musu kwakwalwa. Sai a turo su gaba in za a kai hari, muyi ta kashe su muna kashe su, muna kashe su, mun zaci cewa fada ya kare. Amma daga nan ne masu bakaken kayan zasu fito, wadanda sune nake jin ainihin ‘yan Boko Haram, sai a fara sabon fada.”

“Akwai wani mutumin da yayi ta rokonmu a kan mu kashe dansa a saboda yace idan har ba mu kashe shi ba, to dan zai komo ya kashe shi uban” in ji wannan soja.

Harin da ya kashe mutane fiye da 100 a Jihar Zamfara a watan Afrilu, ya nuna matsala da barazanar yaduwar tashe-tashen hankula zuwa sauran sassan Najeriya. (VOA/Murtala Farouk)

Mike Omeri, darektan Cibiyar Yada Labarai ta Kasa ta Najeriya, wadda gwamnati ta kafa bayan sace ‘yan matan Chibok, yace jami’ai su na sane da wannan bidiyon da wasunsu, amma yace watakila an dauki wannan bidiyon ne a wata kasar Afirka ta Yamma dabam.

“Ba zan iya tabbatar da cewa wadannan sojojin Najeriya ne ba. Rundunar sojojinmu, rundunar sojojin da na sani, ta kwararru ce. Sun je ko ina a duniya, amma ba su yi haka ba,” in ji Omeri.

“Wadannan zarge-zarge na karya ne, wadanda suka fito daga kwakwalwar masu son kai Najeriya su baro. Najeriya kasa ce mai wayewar kai, mai bin dimokuradiyya. Ba zamu yi amfani da gana azaba da tsare mutane haka siddan domin kawo karshen wannan tawaye ba. Mun fuskanci mutanen da muka samu su na karkashe mutane ne kawai, su din ma kama su muka yi, muna musu tambayoyi, su na nan da ransu, ba a kashe su ba,” Omeri ya shaidawa VOA.

Ya kara da cewa, “Rundunar sojojin Najeriya ba zata taba kaskantar da kanta haka ba. Mu ba marasa imani ba ne, ba haka muke ba, a zamanmu na mutane, kuma a zamanmu na rundunar soja.”

Amma kuma ga su sojojin Najeriya, watakila “Hanyar Soja” ita ce hanyar da suke ganin ta fi kaifi ta magance wannan barazana ta ‘yan Boko Haram dake kara yin muni. Sai dai ga wadanda ke kallon wannan lamari daga waje, irin wannan dabarar tana iya haifar da akasin abinda ake son gani: watau zata iya haifar da gaba da kiyayya a zukatan al’umma tare da kara goyon bayan da Boko Haram ke samu.

Kungiyar kare hakkin bil Adama ta Human Rights Watch ta ce “Rundunar JTF tana amfani da karfi fiye da kima, da gana azaba, da tsare mutane a asirce, da yin kwace, da kona gidajen mutane, da satar kudade a lokacin kai farmaki, da kuma kashe mutanen da ta kama ba tare da an gurfanar da su gaban shari’a ba.”

Sarah Margon, shugabar ofishin kungiyar a Washington, ta ce “Ina jin babu shakka cewa irin matakan wuce gona da iri na sojojin Najeriya sun kara ma ‘yan Boko Haram kuzari tare da bakanta sojojin a idanun jama’a farar hula, abubuwan da ba su da amfani ga kokarin kare jama’a da yakar Boko Haram.”

Karin Bayani akan Jini, Hawaye da Fargaba a Daular El-Kanemi >>

XS
SM
MD
LG