Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Shekaru Ashirin da Kisan Kare Dangi a Ruwanda


Bikin tunawa da kashin kare dangi da aka yi a Rwanda inda wasu suka kwanta kamar gawarwaki kamar abun da ya faru a wannan filin shekaru 20 da suka gabata.
Bikin tunawa da kashin kare dangi da aka yi a Rwanda inda wasu suka kwanta kamar gawarwaki kamar abun da ya faru a wannan filin shekaru 20 da suka gabata.

Shekaru ashirin da suka wuce kabilar Hutu ta yi yunkurin kawar da kabilar Tutsi daga doron duniya lamarin da ya lakume rayuka kusan miliyan daya.

Jiya Litinin kasar Rwanda ta cika shekaru ashirin da fara kisan kiyashin alif dari tara da casa'in da hudu daya kashe kimamin mutane dubu tamanin.

A wani biki da aka yi a Kigali baban birnin kasar, shugaban kasar Paul Kagame da baban sakataren Majalisar Dinkin Duniya Banki Moon sun shiga sahun kunna wutar juyayin mutuwar mutane da zaiyi kwanaki dari yana ci.

Kwanaki darin, shine adadin lokacinda yan yakin sa kan kabilar Hutu suka yi barna a duk fadin kasar suka yi ta kashe yan kabilar Tutsi da yan kabilar Hutu masu sausaucin ra'ayi bayan mutuwar shugaban kasar a wani hadarin jirgin sama.

Shugabanin kasashe da jami'an gwamnati daga Amirka da kasashen gabashin Afrika ne suka halarci wannan biki.

A ranar Lahadi baban sakataren Majalisar Dinkin Duniya Mr. Ban yace zai kara jaddada alkawarin kasa da kasa cewa, in Sha Allahu har kasa ta nade ba'a kara yin irin wnnan ta'asa ba.

aka kuma ya yabawa salon mulkin shugaba Kagame, yana mai fadin cewa shugaban ya zama zakaran gwajin dafi.
Wata manhaja mai saukaka wahalar samun gidan abinci na halal ga Musulman dake zaune a kasashen Turai
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:21 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG