Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Gamayyar Kungiyoyin Matasan Arewa ta Karyata Cewa ta Baiwa Shugaba Jonathan Gudumawar Naira Milyan Biyu


Gungun 'yan Najeriya.
Gungun 'yan Najeriya.

Da yake magana kakakin kungiyar komared Bashir Madara yace wanda akace yayi magana a madadin kungiyar basu ma san da zamansa ba.

Gamayyar kungiyoyin matasan Arewa sun nesanta kansu da rahotan dake cewa wai a ranar asabar din data gabata sun bada gudunmawa naira miliyan biyu ga takarar shugaba Goodluck Jonathan, yayin da a hannu guda kuma sukayi Allah wadai da gudunmawar kimanin naira miliyan goma da akace daluban jihar Kano sun baiwa gwamna Rabiu Musa Kwankwaso domin ya sayi form din neman shugabancin najeriya.

Kakakin gamayyar kungiyoyin komorade Bashir Madara, yace basu san da wannan kungiya ko mutumin da yayi magana a amdadinsu ba, saboda baya cikin 'yan gwagwarmaya.

Da yake magana kan haka, wani malamin jami'a Dr. Sa'id Ahmed Dukawa, yace yin haka idan ya tabbata da gaskene, ya sabawa dokar zaben kasa.

Ga karin bayani.

please wait

No media source currently available

0:00 0:03:28 0:00
Shiga Kai Tsaye

Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG