Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Za a Gudanar da Zabuka Cikin Lumana- Nkurunziza


Shugaban kasar Burundi Pierre Nkurunziza
Shugaban kasar Burundi Pierre Nkurunziza

Shugaban kasar Burundi Pierre Nkurunziza ya fadawa kasarsa cewa za a gudanar da zabubbuka dake tafe cikin lumana, ya kuma dage akan cewa rikicin da aka yi kwanan nan a Bujumbura babban birnin kasar, bai dace da halayan dukan ‘yan kasar ba, duk da cewa ana ci gaba da yin zanga-zanga.

Mr. Nkurunziza ya yi wannan jawabin ne a wani gidan talabijin din gwamnati a yammacin jiya Laraba yayin da ya ba da sanarwar cewa za a jinkirta yin zaben ‘yan majalisa da mako guda, wato zuwa ranar 5 ga watan Yuni ke nan saboda tashin hankalin da ake fuskanta.

A makon da ya gabata ne ‘yan adawa suka so su hambarar da gwamnatin shugaban yayin da ya je wani taron kasashen yankin a kasar Tanzania.

Ba a dai sami nasarar yin juyin mulkin ba amma ana ci gaba da samun tashe-tashen hankula.

A yau Alhamis masu zanga-zanga sun yi arangama da ‘yan sanda, inda suka jejjefesu da duwatsu yayin da su kuma jami’an tsaron suka yi amfani da barkonon tsohuwa tare da yin harbin kashedi a iska.

Wadanda suka shaida lamarin sun ce harsashi ya taba akalla mutum daya kuma ta yiwu ma ya mutu.

XS
SM
MD
LG