Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Koriya ta Arewa tana neman saba Alkawari


Korea ta Arewa tace ba zata daina shirinta na kirar makaman nukiliya ba sai lokacin da ta sami kundunan samar da makamashin wutar lantarki ko kuma a bata su. A yau Talata kafofin labarun Korea ta Arewa suka yayata wannan sanarwa. Ba’a tantance dada ko Korea ta Arewar, tana neman kaucewa alkwarin da ta dauka ne a babban taron birnin Beijing na jiya litinin ba. Shugaba Bush na Amurka, ya yaba da alkawarin da Korea ta Arewar tayi jiya litinin a taron kolin, amma yace wajibi ne aje a duba domin tabbatarwa. Korea ta Arewa tace a shirye take ta baiwa jami‘an kasa da kasa damar zuwa su ganarwa idonsu, amma sai an saka mata da agajin tattalin arziki tukuna.

XS
SM
MD
LG