Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Libya Tace Tana Fatar Kyautata Dangantakarta Da Amurka - 2003-08-17


Libya ta ce tana fatar daukar alhakin da ta yi na dasa bam a jirgin saman da ya tarwatse a samaniyar Lockerbie a shekarar 1988, zata kyautata dangantaka a tsakaninta da Amurka.

A cikin hirarrakin da suka yi asabar da kafofin yada labarai na kasashen yammaci, jami'an Libya sun bayyana kwadayin yin aiki tare da Amurka.

A ranar Jumma'a Libya ta rubuta takardar da a ciki ta dauki alhakin dasa bam din da ya tarwatsa jirgin saman kamfanin Pan Am mai lambar tafiya 103, ta kuma yarda zata biya diyyar tsabar kudi dala miliyan dubu 2 da 700 ga iyalan mutane 270 da suka mutu a sanadin wannan lamari.

Amma kuma Libya ta ce ba zata biya karin diyyar ko kwabo ba ga iyalan mutanen da suka mutu a sanadin bam din da aka dasa cikin wani jirgin saman Faransa a 1989, duk ad cewa Faransa ta yi barazanar zata toshe duk wata kafar dage takunkumin da Majalisar Dinkin Duniya ta sanyawa Libya idan har ba ta kara kudin diyyar ba.

XS
SM
MD
LG