Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

An Yiwa Shugaban Guinea Bissau Kisan Gilla


Wasu Sojojin k'asar Guinea Bissau masu bore sun kashe shugaban k'asar Joao Beranrdo Vieira, jim kad'an bayan da wata fashewar bam ta halaka hafsan hafsoshin sojojin k'asar.

Sojoji masu biyayya ga hafsan hafsoshin da aka kashe, Tagme Na Waie, sun farma fadar shugaban k'asa da talatainin dare, sannan su ka harbe shugaba Vieira a lokacin da ya ke k'ok'arin guduwa.

A cikin wata sanarwar da aka gabatar ta kafofin yada labaran gwamnati, rundunar sojojin k'asar sun ce sun shawo kan al'amuran k'asar ta yammacin Afirka, amma rundunar sojojin ta yi kashedin cewa ba fa za ta yarda da abun da ta kira 'yan kwasar ganima da 'yan tayar zaune tsaye ba.

Haka kuma, rundunar sojojin ta ce za ta mutunta kundin tsarin mulki , ta kuma kare demokrad'iya. Kundin tsarin mulki ya yi tanadin cewa shugaban majalisar dokoki Raimundo Perreira shi zai kama ragamar mulki har ya zuwa lokacin da za'a shirya yin zab'e cikin kwanaki 60 wato nan da watanni biyu.

Da safiyar nan ta litinin k'ura ta lafa a Bissau, babban birnin k'asar Guinea-Bissau bayan an kwan dare cikin amon fashe-fashe bama-bamai da b'arin wutar bindigogi.

XS
SM
MD
LG