Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Cheney Ya Zargi Hamas Da Laifin Neman Gurgunta Shawarwarin Wanzarda Zaman Lafiya A Gabas Ta Tsakiya


Mataimakin shugaban Amurka Dick Cheney,yace Hamas tare da goyon bayan Syria da Iran na neman hana shawarwari tsakanin Falasdinu da Isra’ila samun nasara.

Da yake magana da manema labaru yau a birnin kudus,Cheney yace akwai shaida cewa Iran da Syria suna goyon bayan Hamas.Ya zargi kasashen biyu cewa suna kai gwauro su kai mari a cewarsa, wajen ganin sun wargaza shawarwarin wanzar da zaman lafiya da akeyi ahalin yanzu.

Cheney yayi magana ne bayan ya gana da shugaban Isra’ila Ehud Olmert a wata ganawar karin kumallon safe.

A halin yanzu Cheney yana Ankara babban birnin Turkiyya a zango na karshe a rangadin kwanaki tara da ya kai yankin.

XS
SM
MD
LG