Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Sojojin Najeriya Sunyi Arangama Da Tsagerun Niger Delta


Sojojin Nigeria sun tarwatsa gungun 'yan yakin sa-kai na Niger Delta da suka so kai hari akan gidajen ma'aikatan wani kamfanin man fetur.

Jami'an tsaron sunce a jiya Talata ne wadanan mayakan su kamar 20, dauke da makamai kuma a cikin jiragen kwale-kwale masu dan karen gudun tsiya, suka abkawa wannan gidan da ke zaman mazaunin ma'aikatan kamfanin man fetur naExxon Mobil dake Eket a jihar Akwa Ibom.

Jami'an suka ce sun share kamar mintoci 30 suna gwabazawa da mayakan, amma sanarwar kamfanin ExxonMobil din tace ba wanda aka kashe. Hare-hare irin wadanan akan mazaunun ma'aikatu ko kamfunnan man fetur dai abu ne da aka saba das hi sosai a wannan yankin na Niger delta, wanda kamar shine hedkwatar irin wadanan bata-garin.

A inda aka fiton nan, anfi yawan samun irin wannan tashin hankali a jihohin Rivers da Bayelsa, amma a kwanan nan, masu kai harin sun tsanata yawan tada kayar baya a izuwa sassan dake can wajajen inda Nigeria da Cameroon suka yi kan iyaka.

A kwanan baya ne babbar kungiyar 'yan yakin sa-kai ta Niger Delta din, MEND, tace ta janye yarjejeniyar tsagaita wutar da ta kulla da hukumomi, bayanda tayi zargin cewa soja sun kai hari akan wata maboyarta.

XS
SM
MD
LG